✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gwamnatin Kano ta wanke Alhassan Doguwa daga zargin kisan kai

An gaza gamsar da kotu hujjar zargin da ake yi wa Doguwa.

Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Kano ta wanke Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Wakilai, Alhassan Ado Doguwa daga zargin kisan kai da ake tuhumarsa.

Atoni-Janar kuma Kwamishinan Shari’a na jihar, Musa Abdullahi Lawan ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai ranar Alhamis a birnin Dabo.

Lawan ya ce binciken da Ma’aikatar Shari’ar ta gudanar kan tuhumar da ake yi wa Alhassan Doguwa kan laifin kisan, ya nuna cewa ba a same shi da laifin da ake zargi ba.

Kwamishinan ya ce an samu sabani da dama cikin bayanan da aka samu daga wurin shaidu.

Ya kara da cewa, a yayin da suke gudanar da bincike sun gano cewa ma’aikatan asibiti ba su yi cikakken bincike kan mutanen da ake zargin an harba da bindiga ba, soboda haka ba a iya tabbatar da cewa an harbe su ba.

Kwamishinan ya ce an gudanar da bincike kan bindigogi da harsashai da ke hannun ’yan sandan da ke tare da dan majalisar a lokacin da rikicin ya faru.

Sai dai a bayanin nasa babu wata shaida da ta nuna cewa an yi amfani da bindigogin, kasancewar jami’an ’yan sandan sun mayar da daidai adadin harsasan da ke a hannunsu.