✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gobe Najeriya za ta yi wasan sada zumunta da Tunisiya

Hukumar shirya kwallon kafa ta Tunisiya ta amince da yin wasan sada zumunta da kungiyar kwallon kafa ta ’yan kasa da shekara 23 ta Najeriya…

Hukumar shirya kwallon kafa ta Tunisiya ta amince da yin wasan sada zumunta da kungiyar kwallon kafa ta ’yan kasa da shekara 23 ta Najeriya watau (Nigeria’s Under 23) a gobe Asabar a can Tunisiya. Sannan ana sa ran kungiyar U-23 din za ta sake yin wasan sada zumunta da takwararta ta Aljeriya a ranar Laraba mai zuwa.

Bayanin haka na kunshe ne a wata takardar amincewa da wasan da Hukumar FA ta Tunisiya ta aikowa Najeriya a ranar Litinin da ta gabata.
Tuni kocin Tunisiya mai suna Nizar Khanfir ya fitar da jerin sunayen ’yan kwallon da za su fafata da Najeriya a lokacin wasan. Haka shi ma kocin Najeriya Samson Siasia ya fitar da nasa sunayen ’yan kwallon da zai yi amfani da su a wasan.
Haka kuma Siasia ya fitar da jerin ’yan kwallon da za su buga wa Najeriya a gasar sada zumunta ta kasashe shida da za ta gudana a Abuja a tsakanin ranakun 24 ga Fabrairu zuwa 11 ga watan Maris a Abuja.
Ana gudanar da gasar kasashe shida ne daga yankin Afirka a duk bayan shekara biyu kuma wannan karon gasar za ta gudana ne a Abuja.