Aƙalla mutum 95 ne aka tabbatar sun rasu sakamakon girgizar ƙasa da aka samu a ƙasar Tibet.
Wasu mutum 130 sun jikkata a yayin da gine-gine sanda 1,000 suka lalace a cibiyar Ibtila’in da ke yankin Tingri, a cewar kamfanin dillancin labarai na Xinhua na ƙasar China.
A safiyar Talata ce aka samu girgizar ƙasar mai ƙarfin maki 7.1 da faɗin kilomita 10 a yankin Tingri, inda ta yi sanadin rushewar gine-gine.
Girgizar ƙasar ta kai yankin Himalaya da ke kasar Nepal, ind Dutse mafi tsawo a duniya, Everest yake, da kuma Arwa Indiya da ke makwabtaka da Tibet.
- Boko Haram ta mamaye sansanin sojoji ta sace makamai a Borno
- Ɗan ta’adda ya sa wa Zamfarawa harajin N100m
A yayin da ake ci gaba da aikin ceto hukumomi sun dakatar da ayyukan da suka danganci hawa dutsen Everest, hasali ma an rufe sansanin ’yan yawon bude ido da ke shirin hawa dutse.