✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gbajabiamila ya yi ta’aziyyar mutuwar tsohuwar shugabar matan APC, Kemi Nelson

Tsohuwar shugabar matan ta jam'iyyar APC ta rasu a ranar Lahadi.

Shugaban Majalisar Wakilai, Femi Gbajabiamila, ya bayyana alhininsa game da rasuwar Misis Kemi Nelson, wacce ta taba zama shugabar mata ta jam’iyyar APC a yankin Kudu maso Yamma.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, ta hannun mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a, ya bayyana marigayiya Misis Nelson a matsayin daya daga cikin ginshikan jam’iyyar APC a Jihar Legas da Najeriya baki daya, inda ya ayyana mutuwarta a matsayin babban rashi.

Ta kasance tsohuwar kwamishina a Jihar Legas kuma har zuwa rasuwarta, mamba ce a majalisar masu bada shawara ga gwamnan Jihar Legas (GAC).

Nelson, wadda tsohuwar Babbar Darakta ce ta Hukumar Inshora ta Najeriya (NSITF), ta rasu ranar Lahadi tana da shekaru 66 a duniya.