A wannan makon mai karewa ’yan bindiga suka kashe wani babban jami’in soji sannan suka yi awon gaba da maidakinsa.
A makon ne kuma ambaliyar ruwa ta share kaburbura a Babbar Makabartar Gashua a Jihar Yobe.
Ga wadannan, da ma wasu labaran da muka kawo muku, a cikin hotuna.
![SAFRICA-POLITICS-UNREST Wani da ake zargin mai fasa shago ne yana jan wasu kayayyaki a kusa da wani rukunin shaguna da aka barnata a unguwar Vosloorus da ke wajen garin Johannesburg na Afirka ta Kudu ranar 14 ga watan Yuli. Kwana biyar a jere masu fasa shago suka kwashe suna barna duk da sojojin da aka girke don su kwantar da hatsaniyar da ta yi sanadin mutuwar mutum 72 (Hoto: MARCO LONGARI / AFP)](https://i0.wp.com/aminiya.ng/wp-content/uploads/2021/07/A-suspected-looter-pulls-a-few-items-along-scaled.jpg?w=271&h=181&ssl=1)
Wani da ake zargin mai fasa shago ne yana jan wasu kayayyaki a kusa da wani rukunin shaguna da aka barnata a unguwar Vosloorus da ke wajen garin Johannesburg na Afirka ta Kudu ranar 14 ga watan Yuli. Kwana biyar a jere masu fasa shago suka kwashe suna barna duk da sojojin da aka girke don su kwantar da hatsaniyar da ta yi sanadin mutuwar mutum 72 (Hoto: MARCO LONGARI / AFP)