✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ganduje ya biya wa daliban Kano Naira miliyan 300 da ke Sudan

Gwamnan jihar Kano Abdullahi Ganduje ya biya wa daliban jihar Kano alawus na Naira miliyan 300 da ke karatu a jami’ar El-Razi ta birnin Khartoum…

Gwamnan jihar Kano Abdullahi Ganduje ya biya wa daliban jihar Kano alawus na Naira miliyan 300 da ke karatu a jami’ar El-Razi ta birnin Khartoum a Sudan.

Kakakin gwamnatin jihar Kabiru Alhassan Rurum ne bayyana hakan a karshen mako ya kuma ce, ana saran wadanda aka biya kudin, jami’ar zata yaye su a watan Mayu 2019.

Rurum ya ce, akwai dalibai 31 da ke karatu a jami’ar wadanda duk ‘yan asalin jihar Kano ne, 28 na daliban na karatun likitanci yayin da sauran na karatun magunguna da dai sauransu.