✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Dubun barayin sassan jirgin kasa ta cika a Zariya

Ayyukan barayin dai a ’yan kwanakin nan ya jima yana gurgunta harkar sufurin jiragen kasa.

Hukumar Kula da Jiragen Kasa ta Najeriya (NRC) ta tabbatar da kama wasu da ake zargi da satar sassan jirgin kasa a Zariya, jihar Kaduna.

Ofishin hukumar dake kula da Arewacin Najeriya dake garin na Zariya ne ya tabbatar da kamun mutanen a ranar Juma’a.

Ayyukan barayin dai a ’yan kwanakin nan ya jima yana gurgunta harkar sufurin jiragen kasa.

Ko a makon da ya gabata sai da wani jirgin da ya taso daga jihar Legas da nufin zuwa Zariya makare da fayif-fayif na ruwa ya ci karo da makamantan wadannan barayin a Unguwar Kanawa dake Kaduna.

Yayin da yake gabatar da ayarin barayin a Zariya, Injiniyan dake kula da shiyyar Arewa na hukumar, Haruna Sabo ya ce dubun barayin ta cika ne bayan wani ma’aikacin hukumar ya kama su a gundumar Sayi-Dumbi dake hanyar Kaduna zuwa Zariya a ranar Juma’a.

Haruna ya ce dama hukumar ta girke wasu jami’anta domin su ci gaba da yin sintiri a kan titunan jiragen a kullum, yana mai cewa sun dauki matakin ne da nufin kakkabe bata-garin.

“Wadannan jami’an na tsaka da aiki ne sai suka ci karo da wadannan bata-garin suna kwance notuka da karafan da ke rike da jirgin,” inji shi.

Injiniyan ya kuma lura cewa kwance irin wadannan karafa da notukan sune ummul-aba’isun tangardar jiragen, wanda ya ce zai kuma iya haddasa mummunan hatsari.

Ya ce tuni binciken ’yan sanda ya taimaka musu wajen gano masu sayen irin wadannan kayayyakin kuma za a mika su ofishin ’yan sanda na hukumar dake Zariya domin fadada bincike da kuma gano sauran masu hannu a ciki.