A yau ne tsohon dan wasan Najeriya Taiye Taiwo ya cika shekara 34 a duniya. Dan wasan yana cikin ’yan wasan Najeriya da suka dade suna taka leda a kasar waje. Ya buga kwallo a kusan kungiyoyi akalla guda 9 a yankin Turai.
Kungiyoyin da ya buga sun hada da: Marseille, da AC Milan da QPR, da Dynamo Kiev da Bursaspor da HJK Helsinki da Lausanne da AFC Eskilstuna da RoPS.