✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Dan kwallon kasar Ghana ya rasu ana tsaka da wasa

Kafin rasuwar dan wasan an yi masa aiki a zuciyarsa.

Tsohon dan kwallon kasar Ghana, Raphael Dwamena, ya mutu sakamakon bugun zuciya yayin da yake tsaka da buga wasa a kasar Albaniya.

Dan wasan mai shekara 28 ya kasance a gaba wajen zura kwallo a raga a gasar Albaniya a kakar wasa ta bana, inda ya jefa wa kungiyarsa, Egnatia kwallaye tara.

Dwamena ya jefa wa Ghana kwallo tara, amma ya sha fama da ciwon zuciya tsawon rayuwarsa.

A 2017, yunkurinsa komawa kungiyar kwallon kafa ta Brighton ya gagara, bayan ya gaza tsallake matakin gwajin lafiya a kungiyar, kuma a 2021 ya fadi ana tsaka da wasa a Austria.

Mai sharhi kan harkokin kwallon kafa na Albaniya, Endi Tufa, ya ce Dwamena “ya rayu ne don kwallon kafa”.

An yi masa aiki a zuciya a 2020, inda aka dasa na’ura don ba shi damar ci gaba da murza leda.

Bayan yi masa aiki, ya koma taka leda a gasar Danish, Austria, da Swiss kafin daga bisani ya koma kungiyar Albaniya KF Egnatia a watan Janairun bana.

Hukumar kwallon kafa ta Albaniya ta ce mutuwarsa ta girgiza harkar kwallon kafar kasar kuma ta dage duk wasannin da aka shirya yi a kasar a wannan mako.