✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Buratai ya bukaci sojoji su gaggauta murkushe ’yan ta’addanci

Buratai ya kara kira a gare su da su kokarta su muttsike matsalar, kar ta samu gindin zama kamar yadda aka gani a kasashen Sri…

Tsohon Babban Hafsah Sojin Kasan Najeriya, Tukur Yusuf Buratai, ya yi kira ga shugabannin soji sun hanyarta kawo karshen ayyukan ta’addanci a yankin Tafkin Chadi.

Laftanar-Janar Buratai mai ritaya ya yi wannan kira ne a Taron Kasa da Kasa na Farko da Sashen Binciken Tarihi da Dabaru na Jami’ar Maiduguri ya gudanar a Jihar Borno.

Da yake jinjina wa sojoji da sauran jami’an tsaro bisa kokarinsu da yadda suke sayar da rayukansu wajen murkushe kungiyoyin ta’addanci, Buratai ya kara kira a gare su da su kokarta su muttsike matsalar, kar ta samu gindin zama kamar yadda aka gani a kasashen Sri Lanka da Columbia.

“Muna ganin ya kamata a kammala yakin nan da lokaci, kar a bari ya tsawaita kamar na kasashen Columbia da Sri Lanka,” in ji Buratai.

Ya jaddada muhimmancin hadin kai tsakanin sojoji da sauran hukumomin tsaro wajen dakile ayyukan laifi da samar da tsaron rayuka da dukiyoyi.

Da haka ne a cewarsa, cikin wata biyar sojoji suka yi nasarar kwace kananan hukumomi tara daga hannun ’yan ta’adda a Jihar Borno a zamanin jagorancinsa.

A jawabinsa, Shugaban Jami’ar Maiduguri, Farfesa Aliyu Shugaba, ya ce jami’ar ba ta ba da kai bori ya hau ba wajen dakatar da harkokinta, duk kuwa da hare-haren kunar bakin wake hudu da kungiyar Boko Haram ta kai jami’ar.