✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Brazil za ta kece raini da Najeriya

kasar Brazil ta amince da ta yi wasan sada zumunta da Najeriya a matakin ’yan kasa da shekara 23 (U-23).  Ana sa ran wasan zai…

kasar Brazil ta amince da ta yi wasan sada zumunta da Najeriya a matakin ’yan kasa da shekara 23 (U-23).  Ana sa ran wasan zai gudana ne a ranar 23 ga wannan wata da muke ciki a filin wasa na Kleber Andrade da ke Brazil.
Brazil ta sanar da haka ne a wata takarda da ta rubutowa Hukumar shirya kwallon kafa ta kasa (NFF) a karshen makon jiya.
Brazil ta ce ta shirya wannan wasa na sada zumunci ne a kokarin tunkarar gasar Olamfik da za a yi a kasar a watan Agustan wannan shekara, inda Brazil da Najeriya na daga cikin kasashen da za su fafata a bangaren kwallon kafa yayin gasar.
Idan za a tuna a shekarar 1996 ce Najeriya ta fitar da Brazil a matakin kusa da na karshe (Semi-Fainal) a gasar Olamfik da ta gudana a Atlanta na Amurka. Ana saura minti 15 a tashi wasan ne Najeriya ta fanshe ci 3-1 da Brazil ta yi mata, kuma bayan an kara lokaci ne Najeriya ta sake jefa kwallo a ragar Brazil da hakan ya sa ta fitar da ita a gasar.
A wasan karshe (fainal) Najeriya ta sake doke Ajantina da ci 2-1 da hakan ya sa ta lashe lambar zinare a bangaren kwallon kafa.  Hakan ya sa ta zama kasar Afirka ta farko a tarihin gasar a wancan lokaci da ta taba kai wa wannan matsayi.
Tun lokacin ne Brazil take mamakin yadda Najeriya ta samu nasara a kanta duk da zaratan ’yan kwallon da take ji da su irin su Bebeto a wancan lokaci.
Masana harkar kwallo suna ganin Brazil ta shirya wannan wasa ne don tabbatar da sahihancin ’yan kwallonta kafin watan Agustan wannan shekara da za a fara gasar Olamfik a kasar.
Koci Samson Siasia ne zai jagoranci kungiyar a gasar ta Olamfik kuma ana sa ran zai gayyato zaratan ’yan kwallo irin su Kelechi Iheanacho da sauransu a wasan na sada zumunci.