✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Bidiyon Dala: Ganduje ya sake maka Jafar Jafar a kotu

Gwamnan ya sake maka shi a kotu kan zargin bata masa da yake yi.

Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ya sake maka mawallafin jaridar intanet ta DAILY NIGERIAN, Jafar Jafar a kotu.

A watan Oktoban 2018 ne dan jaridar ya saki wasu bidiyo na zargin Gwamnan Kanon da karbar rashawa a hannun wasu ’yan kwangila a jihar.

Lamarin da ya tada kura a sassan Najeriya ya sa gwamnan maka Jafar a kotu don ta bi masa kadinsa kan abin da ya kira cin mutunci da bata suna.

Bayan daukar lokaci ana shari’a, gwamnan ya janye karar da ya shigar, inda a ranar 6 ga watan Yuli, 2021 kotun ta umarce shi ya biya dan jaridar N800,000 saboda bata masa lokaci da ya yi.

Sai dai a ranar 15 ga Yuli, 2021 Ganduje ya sake maka Jafar a wata Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja.

An aike wa dan jaridar takardar sammaci ana bukatar ya bayyana a gaban kotun cikin makonni biyu masu zuwa.

A baya, Jafar Jafar, ya maka Ganduje a kotu yana neman a biya shi N3,000,000 kan barazana da bata suna da Gwamnatin Kano ta yi masa.