Wani malami mai suna Malam Muhammad Auwal Abubakar da ake wa lakabi da Maiguduma, ya yi Allah wadai da wani faifai da ke yawo a kasuwa inda a cikinsa wani malami mai suna Malam Sanusi Khalil ya ce dogarin marigayi Shugaban kasa Janar Sani Abacha, Manjo Hamza Al-Mustapha na horar da matasa dubu daya, don auka wa masu hamayya da Shugaban Goodluck Jonathan kafin zaben 2015, inda ya bayyana hakan a matsayin kazafi da ya saba wa shari’an Musulunci da dokar kasa.
Malam Maiguduma wanda ya bayyana haka a yayin zantawa da Aminiya, ya ce danganta Manjo Al-Mustapha da al’amarin idan ma har akwai shirin yin hakan, wani makirci ne da bi-ta-da-kulli da wasu da ke adawa da fitowarsa daga gidan kurkuku, suka kitsa da kuma ke da nasaba da siyasa. Ya ce ba daidai ba ne malami ya tsunduma kansa a ciki, inda ya bukaci al’ummar Musulmi da Kiristoci musamman talakawa su dawo daga rakiyar amfani da addini ko malamai wajen biyan bukatar siyasa, ya ce siyasar kasar nan ba ta ginu a kan tsarin addini ba.
Malamin ya ce abin da ya kamata talakawa mabiya addinan biyu su maida hankalinsu a kai shi ne zaben adalan shugabanni, sannan su yi watsi da azzulumai koda ’yan uwansu ne.
Bayanin da wani malami ke yi cewa Al-Mustapha zai horar da makasa kazafi ne – Maiguduma
Wani malami mai suna Malam Muhammad Auwal Abubakar da ake wa lakabi da Maiguduma, ya yi Allah wadai da wani faifai da ke yawo a…
