✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Barau ya gabatar da kudurin neman kafa Hukumar Raya Arewa maso Yamma a Majalisa

Sanatan Kano ta Arewa, Barau Jibrin ne ya gabatar da kudurin

Kudurin neman kafa Hukumar Raya Yankin Arewa maso Yamma (NWDC), wanda Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin ya gabatar, ya tsallake karatu na farko a Majalisar.

Kudurin mai taken, bukatar kafa Hukumar Raya Yankin Arewa maso Yamma, 2023, ya tsallake karatu na farko ne a zaman majalisar na ranar Talata wanda aka yi a karkashin jagorancin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio.

Akawun Majalisar Dattawa, Barista Chinedu Akubueze ne ya karanta taken kudurin a takaice a lokacin zaman.

A wata sanarwa daga sashen yada labarai na ofishin Mataimakin Shugaban Majalisar, an bayyana cewa idan aka kafa hukumar, za ta taimaka wajen kawo ci gaban yankin na Arewa maso Yamma mai jihohi bakwai; Kano, Kaduna, Kebbi, Katsina, Jigawa, Sokoto da Zamfara.

Haka kuma, idan aka kafa ta, hukumar za ta samo kudaden da za ta yi amfani da su wajen inganta harkokin noma da kasuwanci a yankin.

A shekara 10 da suka gabata, yankin na Arewa maso Yamma, musamman jihohin Kaduna da Katsina da Sokoto da Zamfara sun sha fama da matsalar rashin tsaro, wanda hakan ya taimaka wajen kawo tsaiko ga ci gaban yankin.

Idan aka kafa hukumar, za ta fi mayar da hankali wajen samar da ci gaban yankin na Arewa maso Yamma, musamman a bangaren noma da kiwo, samar da gidaje, raya karkara, samar da wutar lantarki da ruwan sha da bunkasar kasuwanci.

Da sannu za a gabatar da kudurin domin karatu na biyu.