✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Bafarawa ya kaurace wa taron zaben PDP a Sakkwato

Bafarawa bai gamsu da rabon mukaman sabbin shugabannin PDP ba a Sakkwato

Tsohon Gwamnan Jihar Sakkwato Attahiru Dalhatu Bafarawa bai halarci taron zaben shugabannin Jam’iyar PDP da ake gudanarwa a filin Wasa na Giginya a birnin Sakkwato.

Tun kafin soma fara taron an yi ta rade-radin cewa Bafarawa ba zai halarta ba.

Majiyarmu ta ce Bafarawa ya kaurace wa taron ne saboda bai gamsu da yadda yadda aka raba mukaman sabbin shugabannin jam’iyyar da aka yi ta kai ruwa rana da shi a kai ba.

Karin bayani na tafe…