✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ba zan bar PDP ba ko na fadi zaben fidda gwani- Kwankwaso

Tsohon Gwamnan Jihar Kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya ce ko da ya fadi zaben fidda gwani, ba zai bar PDP ba. Sanata Kwankwaso ya…

Tsohon Gwamnan Jihar Kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya ce ko da ya fadi zaben fidda gwani, ba zai bar PDP ba.

Sanata Kwankwaso ya bayyana hakan ne a ofishin Jam’iyyar PDP a lokacin da ya je karbi fom din tsayawa takara a sakatariyar ofishin a Abuja.

“Yarjejeniya a fitar dad an takara shi ya fi kyau, amma wasu ‘yan takara sun fi son zaben fidda gwani. Idan shugabanni jam’iyya suka ce ga wanda suke so, zan yi biyayya.”