Hukumar kwastan ta kasa ta ce rudanin da ya barke tsakaninta da mutanen garin Badagry, wanda har ya yi musabbabin mutuwar daya daga jami’anta mai suna John Motojehi ba zai sa ta gaza a gudanar da ayyukanta ba.
Mataimakin shugaban hukumar mai kula da shiyyar A, Mista bictor Gbemuda ne ya yi wannan kalamin sa’ilin da yake wa manema labarai jawabi bayan ya wakilci shugaban kwastan din wajen ta’aziyyar mamacin, biyo bayan tashin hankalin da ya barke tsakanin wasu ’yan simoga da jami’an kwastan da ke bakin iyakar Najeriya da Jamhuriyar Benin.
Ya ce hukumar tana jimamin rasuwar jami’in wanda ’yan fasa kwaurin suka yi wa taron dangi ne har daga bisani suka kona motar da yake ciki sa’ilin da yake kan hanyarsa ta zuwa bakin aiki.
Mista Gbemuda ya ce an kame wasu daga cikin wadanda ake tuhuma da aikata wannan danyen aikin, kuma za a ci gaba da bincike har sai an gano wadanda ke da hannu ciki kuma hukumar ba za ta kyale ba, sai ta ga an yi adalci, domin haka ya zame darasi ga masu tunanin aikata irin haka.
Dangane da ko akwai wani tsari da hukumar ta yi ko kuma za ta yi domin ganin haka bai sake faruwa ba, mataimakin shugaban ya ce za su kara inganta dangantakarsu ne da mutanen da suke zaune tare da su domin su kara fahimtar juna, kuma batun yin sako-sako da aikinsu bai ma taso ba, sai ma dai su kara kaimi.
Mista bictor ya ce zuwansa gidan marigayin wata manuniya ce ga sauran jami’an cewa wanda duk ke aikinsa kuma wani abu ya same shi ko da ba mutuwa ba ne ya san yana da goyon bayan hukumar, don haka ya yi kira ga jami’an na kwastan duk inda suke cikin Najeriya su kara kaimi wajen tafiyr da aikinsu.
Daga karshe ya ce hukumar za ta dauki nauyin karatun ’ya’yan marigayin har zuwa jami’a kuma a kowace makaranta suke son zuwa, kuma ta yi alkawarin daukan dawainiyar iyalinsa.
Ba za mu gaza a wajen gudanar da aikinmu ba Inji ACG Victor Gbemudu
Hukumar kwastan ta kasa ta ce rudanin da ya barke tsakaninta da mutanen garin Badagry, wanda har ya yi musabbabin mutuwar daya daga jami’anta mai…
