Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da matar Mataimakin Akanta- Janar na jihar Katsina Hajiya Lubabatu Sani Lawal BK bayan sun shiga cikin gidanta.
Majiyarmu ta samu rahotan cewa, ‘yan bindigar da suka su kimanin goma sun shiga cikin gidan Hajiya Lubabatu, ne da yake unguwar rukunin gidajen gwamnati da misalin karfe 9 na dare ranar Laraba.
Rahotan na bayyana cewa, ‘yan bindigar sun shiga gidan da kananan motoci biyu daya kirar 206, sannan suka fara dukan wasu da ke cikin gidan sannan suka binciko inda take suka sace.
Har zuwa yanzu masu garkuwan ba su kira ba don neman kudin fansa kafin a sako Hajiya Lubabatu.