✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An yanke wa ’yan kungiyar IS 17 hukuncin kisa a Libya

Ana zargin mutanen ne da hannu a kisan mutane fiye 50 da kuma sace wasu dama

Wata kotu a kasar Libya ta yanke wa wasu ’yan kungiyar IS su 17 hukuncin kisa.

Dukkansu an same su da aikata laifuffuka a lokacin da masu ikirarin jihadi suke da iko da Yammacin Sabratha.

Ofishin Babban Mai shari’a na kasar ya ce mutanen na da hannu a kisan mutane fiye 50 da kuma sace wasu dama.

Kungiyar IS ta kwace ikon wasu yankunan Sabratha a 2014, kafin daga bisani ta kwace ikon birnin Sirte, wanda ya zamo matattarar masu ikirarin jihadin a Libya.

Bayan shekara biyu da kwace ikon, sojojin Libya da ke biyayya ga gwamnatin kasar sun fatattake su daga birnin.(RFI)