✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An koro daliban Najeriya da ke karatu a Birtaniya

Tashin Dala ya sa ’yan Najeriya kasa biyan kudin makaranta, lamarin da ya sa aka koro su gida daga Birtaniya

Mummunan karyewar darajar Naira ya shafi daliban Najeriya da ke karatu a Jami’ar Teesside da ke kasar Birtaniya.

Kawo yanzu dai  Jami’ar Teesside ta kado keyar daliban da suka kasa biyan kudin makaranta.

Wasu daga cikin daliban sun shaida wa BBC cewa sun ji takaicin abin da jami’ar ta yi na rashin kulawa da matsalolinsu.

Duk da koke-koke da kokarin da daliban suka yi na yin shawarwari da tsare-tsare na biyan kudin, jami’ar ta kaddamar da tsauraran ka’idojin biza, lamarin da ya sa aka rufe asusun daliban aka kuma soke bizarsu.

Jami’ar ta ce rashin biyan kuɗin makarantar ya saba wa sharuddan bizar da aka ba wa daliban.

Daliban da abin ya shafa sun ce suna cikin tsananin damuwa sakamakon ƙin taimaka musu da jami’ar ta yi; duk da iƙirarin jami’ar ta yi na bayar da taimako ga wasu daga cikinsu.