✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An karrama Buhari da lambar yabo mafi daraja ta Nijar

Buhari ya zama zakaran gwajin dafi a cikin shugabannin Afrika.

Shugaban jamhuriyyar Nijar mai barin gado, Mahamadou Issofou, ya karrama Shugaba Muhammadu Buhari da lambar yabo mafi girma ta kasar Nijar saboda rawar da gwamnatinsa ta taka wajen inganta huldar da ke tsakanin kasashen biyu.

Wannan na zuwa yayin da Shugaba Issofou ya kai ziyarar aiki a Najeriya inda ya gana da Shugaba Buhari a fadarsa da ke Abuja a ranar Talata.

Shugaban Issofou ya yaba wa Najeriya musamman a kan dangartakar da ke tsakanin kasashen biyu da kuma hadin gwiwar da ke tsakaninsu a fagen yaki da ’yan ta’adda da suka uzzura wa kasashen biyu.

Daga bisani Shugaba Issofou wanda zai sauka daga mulki a watan gobe, ya kaddamar da wata hanyar da aka sanya sunansa a Abuja, inda ya samu rakiyar Gwamnonin Jihohin Kebbi, Zamfara, Katsina, Jigawa, Sakkwato, Kano da Yobe.

A nasa jawaban, Shugaba Buhari ya yaba wa takwaran nasa dangane da salon jagorancinsa na yaki da talauci a tsakanin al’umma.

Kazalika, Buhari ya yaba wa Shugaba Issofou kan tsayuwar dakan da ya yi ta kin amincewa da sauya kundin tsarin mulkin kasar da zai bashi damar ci gaba da kasancewa a kan gado na mulki.

A baya bayan nan ne Shugaba Issofou ya lashe lambar girma ta Gidauniyar Mo Ibrahim mai dauke da kyautar Dala Miliyan biyar saboda nagartar da ya nuna yayin jagorancin kasarsa.