✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An garzaya da ’yan Isra’ila 154 asibiti bayan harin Iran

Ma'aikatar lafiyar Isra'ila ta ce wasu daga cikin majinyatan suna cikin halin rai-kwakwai-mutu-kwakwai

Isra’ila ta tabbatar cewa an garzaya da ’yan ƙasarta aƙalla 154 asibiti bayan sabbin hare-haren ramuwar gayya da Iran ta kawo mata.

Ma’aikatar lafiyar Isra’ila ta ce aƙalla mutum huɗu daga cikin waɗanda aka kai asibitin suna cikin halin rai-kwakwai-mutu-kwakwai, wasu biyar kuma na samun kulawa ta musamman saboda tsananin tashin hankali.

Alkaluman da ma’aikatar ta fitar sun nuna cewa mutum 130 daga cikin majinyatan sun samu raunuka marasa tsanani a sakamakon hare-haren.

Wannnan na zuwa ne a yayin da Iran ta ci gaba luguden rokoki a matsayin ramuwar gayya a sassan Isra’ila a a ranar Talata.

Isra’ila ta ce Iran ta lashe mata mutane akalla 24.

A ɗaya ɓangaren kuma Iran cewa harin tsokana da Isra’ila ta kai mata ya yi ajalin kimanin mutum 224.