✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An cafke malami kan cakuda mata da maza a sahun Sallah

Malamin da ya halasta wa mata yin huduba da limancin sallar Juma'a yana fuskantar zargin yada akidun da suka saba wa Musulunci

Hukuma ta cafke wani mai wa’azin Musulunci kuma shugaban makarantar addini kan laifin batanci ga addinin Islama da kuma cakuda mata da maza a sahun Sallah a kasar Indonesia.

Malamin mai suna Panji Gumilang, yana kuma fuskantar zargin halasta wa mata yin huduba da limancin Sallar Juma’a makarantar kwana ta Musulunci mai suna Al-Zaytun da yake jagoranta.

Fitar wani bidiyo da ke nuna mata da maza suna sallah a sahu daya a makarantar mai dalibai 5,000 a watan Afrilu ya jawo tofin Allah tsine da bore a kusa da harabar makarantar, lamarin da ya sa jami’an tsaro suka cafke shi.

Addinin Musulunci dai ya haramta cakuduwar maza da mata, inda a sallah sahun mata ke kasancewa daban, kuma a bayan na maza; haka bai halasta wa mata huduba ko jagorancin sallar Juma’a ba.

Al’ummar kasar Indonesia wadanda yawancinsu Musulmi ne, na zargin makarantar Al-Zaytun da yada akidun da suka ci karo da koyarwa Al-Kur’ani da sunan Musulunci.

Malamain da ke tsare a hannun ’yan sanda a yanzu yana fuskantar zargin batanci, maganganun tsana da kuma yada akidun da suka saba wa koyarwar Al-Kur’ani da sunan Musulunci a makarantar.

Kakakin ’yan sandan kasar Ahmad Ramadhan ya sanar a ranar Laraba cewa sun cafke shugaban makarantar, Panji Gumilang, inda suka tsare shi na tsawon kwana 20, gabanin gurfanar da shi a gaban kotu.

Idan kotu ta sami Gumilang da laifi, za a yanke masa hukuncin daurin shekara 21 a gidan yari — 5 kan batanci, 6 na yada maganganun tsana da kuma 10 a kan tayar da zaune tsaye da gangan.

Ana kuma zargin Gumilang da makarantarsa da alaka da kungiyar Darul Islam, da ta yi yakin kafa gwamnatin Musukunci a kasar a shekarun 1950 zuwa 1960.

Tun a watan Yuni dubban mutane sun sha yin zanga-zangar neman a rufe makarantar da ke yankin Yammacin Java.

Kundin tsarin mulkin kasar Indonesia wadda yawancin al’ummarta Musulmi ne ya yi tanadin hukunci ga masu aikata batancin addini.

Sai dai a baya ba a fiye amfani da dokar ba, sai bayan mulkin soji a 1998, inda a shekarar 2017 aka yanke hukuncin daurin shekara biyu ga tsohon gwamnan birnin Jakarta na farko, wanda Kirista ne.