✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ambaliya ta raba mutum 2,000 da gidajensu a Sakkwato

Akalla mutane 1,700 da gonaki hekta 600 abun ya shafa a Karamar Hukumar Gada

Kimanin mutane 2,000 sun rasa gidajensu sakamakon ambaliya a al’ummomi daban-daban na kananan hukumomin Gada da Dange-Shuni da ke Jihar Sakkwato.

Daraktan Bada Agaji a Hukumar Agajin Gaggawa ta Jihar Sakkwato (SEMA), Mustapha Umar, ya bayyana cewa ambaliyar ta shanye gidaje da gonaki da dama a yankunan.

Ya kara da cewa kimanin mutane 1,700 ne abun ibtilia’in ya shafa a Karamar Hukumar Gada, inda abin ya shanye kimanin hekta 600 na filayen noma baya ga asarar dabbobi da kayan abinci masu yawan gakse.

Ya lissafa yankunan da abin ya shafa a Karamar Hukumar Gada da suka hada da Dantudu da Balakozo da Gidan Tudu da kuam Tsitse.

Sai dai ya bayyana cewa hukumar na ci gaba da bincike kan ibtila’in na Dange-Shuni domin tantance adadin mutanen da abin ya shafa da kuma girman barnar a kararamar hukumar.

A daidai lokacin, jigo a Jam’iyyar APC kuma dan Majalisar Mattijai daga Sokkwato ta Arewa, Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko, ya jajanta wa wadanda abun ya shafa.

A sanarwa da kakakinsa, Bashar Abubakar, ya fitar, Sanata Wammako, ya yi musu addu’a tare da rokon Allah kawo musu dauki.