✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Abin da ya sa aka kara mana wa’adi- Shugaban APC na kasa

Shugaban Jam’iyyar APC na kasa, John Odigie-Oyegun ya ce majalisar koli ta jam’iyar ta kara musu wa’adin shugabanci ne da kyakkyawar niyya. Shugaban jam’iyyar ya…

Shugaban Jam’iyyar APC na kasa, John Odigie-Oyegun ya ce majalisar koli ta jam’iyar ta kara musu wa’adin shugabanci ne da kyakkyawar niyya.

Shugaban jam’iyyar ya yi wannan jawabin ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Abuja.

Oyegun ya kara da cewa an yanke shawarar kara wa shugabannin jam’iyyar a duk mataki wa’adi ne domin su samu damar gyara-gyare domin fuskanta kalubalen da ke gabansu musamman zaben 2019 da ke tafe.