✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Abba Gida-Gida ya naɗa sabon Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Kano

An tabbatar da kwarewarsa a ma’aikatun gwamnatin Kano daban-daban da ya yi aiki tsawon shekaru fiye da talatin.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya naɗa Alhaji Abdullahi Musa a matsayin sabon Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar Kano.

Wannan dai na kunshe ne cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Harkokin Labarai na Fadar Gwamnatin Kano, Sanusi Bature Dawakin-Tofa ya fitar a wannan Litinin din.

Hakan dai ya biyo bayan ajiye aiki da tsohon Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Kano, Alhaji Usman Bala mni ya yi a wannan wata na Nuwamba.

Dawakin-Tofa ya ce sabon Shugaban Ma’aikatan gogaggen ma’aikacin gwamnati ne wanda aka tabbatar da kwarewarsa a ma’aikatu, hukumomi da cibiyoyin gwamnatin Kano daban-daban da ya yi aiki tsawon shekaru fiye da talatin.

Alhaji Abdullahi wanda ya fito daga Karamar Hukumar Kiru, ya yi aiki a fannoni da dama ciki har da Babban Sakatare a Fadar Gwamnatin Kano, Cibiyar Kula da Harkokin Gwamnati, Ma’aikatar Ayyuka na Musamman da Hukumar Servicom.

Ya samu shaidar digiri na farko a fannin nazarin harkokin diflomasiyya daga Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya.

Haka nan, ya samu shaidar digiri na biyu a fannin Tsare-Tsare da Gudanarwa daga Jami’ar Bayero da ke Kano, da kuma karin wata shaidar digiri na biyu a fannin nazarin Dabarun Tsaro a Harkokin Gudanarwa daga Makarantar Horas da Dakarun Soji (NDA) da ke Kaduna.

Sanarwar ta kara da cewa, Gwamna Abba Yusuf wanda ake yiwa lakabi da Abba Gida-Gida, ya buƙaci sabon Shugaban Ma’aikatan da ya sauke nauyin da rataya a wuyansa bisa la’akari da tsare-tsare da dokokin aikin gwamnati.