✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
  • Trust Radio
  • Trust TV
  • Teen Trust
  • Dailytrust
  • Nigeria Daily
  • Najeriya a Yau
Bincika
Gida - Dailytrust Aminiya
Yi Rajista
  • Gida
  • Labarai
  • Saurari Shirye-Shiryenmu
  • Bidiyo
  • Fagen Siyasa
  • Al'ajabi
  • Dandalin Nishadi
  • Aminyar Kurmi
  • Kasuwanci
  • Wasanni
  • Kasashen Waje
  • ☰
Click Here To Listen To Trust Radio Live
Addini

A yawaita addu’o’i a Sabuwar Shekarar Musulunci —Sultan

Mai Alfarma sakin Musulmi Muhamad Sa’ad Abubakar ya bukaci al’ummar Musulmi a Najeriya da su kara neman kusanci da Allah da kuma yawaita addu’o’i. Sarkin…

Muhammad Sa’ad Abubakar III, Sarkin Musulmin Najeriya.
    Daga Sagir Kano Saleh
Thu, 20 Aug 2020 15:12:26 GMT+0100

Mai Alfarma sakin Musulmi Muhamad Sa’ad Abubakar ya bukaci al’ummar Musulmi a Najeriya da su kara neman kusanci da Allah da kuma yawaita addu’o’i.

Sarkin Musulmi ya yi kiran ne yayin ayyana Juma’a 21 ga watan Agustan 2020, a matsayin ranar 1 ga watan Muharram na Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1442 Bayan Hijira.

Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci a Najeriya NSCIA, ta bayyana haka a ranar Alhamis ta bakin Mataimakin Babban Sakatarenta, Farfesa Salihu Shehu.

Ya ce babu tabbacin ganin watan Muharam a duban farko da aka yi ranar Laraba, wadda ita ce 29 ga watan Zhul Hajji, 1441 Bayan Hijira.

“Saboda haka, Shugaban NSCIA, Mai Alfarma Sarkin Musulmi ya amince da ranar Juma’a 21 ga Agusta, 2020 a mats—ayin ranar 1 ga Muharram, 1442 Hijiriyya.

“Majalisar na kira ga al’ummar Musulmin Najeriya da su ci gaba da wanzar da zaman lafiya da hadin kai tsakanin dukkan ‘yan kasa.

Sarin Musulmin ya kuma yai wa Musulmi fatar za a shiga sabuwar shekarar lafiya, tare da kiran su da su kara dagewa wajen ibada da addu’o’in neman Allah Ya kawo karshen annobar coronavirus.

Share this:

  • Click to share on Facebook (Opens in new window) Facebook
  • Click to share on X (Opens in new window) X

Like this:

Like Loading...

Related

  • Musulmi
  • Najeriya
  • NCSCIA
  • Sabuwar shekara
  • Sarkin Musulmi
Karin Labarai
  • 1 week ago
    Gwamnatin Kano ta ba da hutun sabuwar shekarar musulunci
    Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf
  • 1 week ago
    Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Muharram
    Sarkin Musulmi Muhammad Sa'ad Abubakar
  • 2 weeks ago
    ’Yan Najeriya da suka maƙale a Isra’ila na neman ɗauki
  • 2 weeks ago
    Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia
  • SPONSOR AD

    BIBIYE MU AMINIYA

    • Gida
    • About Us
    • Contact Us
    • Trust +
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Terms of Use
    • Business Directory
    • 20 P.O.W Mafemi Crescent, Utako District, Abuja
    • 700-177-7577
    • [email protected]
    1998 - 2021 Media Trust Limited. All rights reserved.
    %d