Najeriya ta tura sojojinta 197 domin zuwa aikin tabbatar da tsaro da wanzar da zaman lafiya a kasar Gambia.
Dakarun na Najeriya waɗanda tuni suka kammala samun horo, za sai yi aikin wanzar da zaman lafiya a Gambia be a ƙarƙashin rundunar Ƙungiyar Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS) da sunan (ECOMIG).
Shugaban Ayyuka na Rundunar Sojin Ƙasa ta Najeriya, Manjo-Janar Uwem Bassey, ya buƙaci sojojin da su kasance masu nuna nuna ƙwarewa da jarumta a yayin gudanar da ayyukansu a ƙasar Gambia.
Ya yi wannan kira ne a jawabinsa a wurin bikin yaye sojojin a Barikin Sojoji na Jaji da ke Jihar Kaduna, kafin tafiyarsu.
- Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila
- An sallami ƙarin ma’aikata 639 a tashar Muryar Amurka
Manjo-Janar Bassey ya buƙaci sojojin da su guji nuna son kai, su mutunta hakkokin ɗan Adam da kuma dokoki da al’adun al’ummar Gambia.
Ya gargaɗe su game da cin zarafi musamman na jinsi, tare da cewa duk sojan aka samu da laifi zai gamu da tsauraran matakan ladabtarwa.
Bassey ya bayyana cewa Najeriya tana da dogon tarihi na bayar da gudummawa ga ayyukan wanzar da zaman lafiya na ƙasar da ƙasa, inda sojojinta ke samun karɓuwa a duniya saboda jaruntakarsu, da ƙwarewarsu.
Sojojin Najeriya sun taka muhimmiyar rawa wajen dawo da zaman lafiya a rikice-rikicen da aka samu a faɗin Afirka da ma duniya, ciki har da Lebanon da Yugoslavia da Laberiya, Saliyo, da Sudan, inda suka ci gaba da samun yabo saboda jaruntakarsu da ƙwarewarsu.