✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Za a fara shari’ar ’yan Boko Haram 1,670

Ministan Shari’a na Najeriya, Abubakar Malami ya ce za a fara shari’ar ’yan kungiyar Boko Haram da aka kama a ranar Litinin, wacce ta yi…

Ministan Shari’a na Najeriya, Abubakar Malami ya ce za a fara shari’ar ’yan kungiyar Boko Haram da aka kama a ranar Litinin, wacce ta yi daidai da tara ga watan Oktoban shekarar da muke ciki.
A wata sanarwa da mai magana da yawunsa ya fitar, Othman Salihu Isah, jiya, ministan ya bayyana cewa  ’yan Boko Haram dubu daya da dari shida da saba’in wadanda ake tsare da su a wuri na musamman da ke garin Ka’inji a jihar Neja za su kasance na farko da za a fara shar’arsu.
Ya ce babban jojin gwamnatin tarayya ya nada alkalai hudu da za su saurari shari’ar.
Ya bayyana cewa Ministan Shari’ar ya amince da jerin  sunayen masu gabatar da kara da za su gabatar da kararrakin a kotu.