✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

‘Yan Najeriya ku zabi ‘yan takara masu gaskiya – Buhari

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bukaci ‘yan Najeriya da su zabi ‘yan takara masu gaskiya da rikon amana a zaben shekarar 2019. Shugaban wanda sakataren…

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bukaci ‘yan Najeriya da su zabi ‘yan takara masu gaskiya da rikon amana a zaben shekarar 2019.

Shugaban wanda sakataren asusun kula da manyan makarantu (TETFund), Dakta Abdullahi Baffa Bichi ya wakilta a taron Maukibi na mabiya darikar Qadiriyya da aka yi a karshen mako a Kano.

Shugaba Buhari ya ce, masu kada kuri’a suna da muhimmiyar rawar da zasu ta ka wajen yakar cin hanci da rashawa a duk matakan gwamnati.