✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan kungiyar asiri sun kashe masu shirin tafiya NYSC a Bayelsa

sun rasu ne bayan da gungun wasu mutane da ke wake-waken kungiyar asiri a cikin wata mota suka kai musu hari da adduna.

Wasu daliban jami’a da ke shirin tafiya aikin yi wa kasa hidima NYSC sun rasu a wani harin da ake zargin ’yan kungiyar asiri ne suka kai musu a yankin Gbarabtoru-Ekpetiama, Karamar Hukumar Yenagoa.

Matasan biyu da suka kammala karatunsu a Jami’ar Niger Delta (NDU), Amassomma, sun rasu ne bayan da gungun wasu mutane da ke wake-waken kungiyar asiri a cikin wata mota suka kai musu hari da adduna.

Kwamandan Kungiyar ‘Yan Banga (VGN) na Jihar Bayelsa,Tolummbofa Akpoebibo Jonathan ya ce, daya daga cikin samarin ya yi kokarin tserewa, amma maharan suka bi shi suka kama shi suka sassare shi.

Ya bayyana cewa da misalin karfe 11:00 na daren ranar Alhamis ne, abin ya faru kuma matasan biyu biyu sun mutu ne sakamakon raunukan da suka samu.

Kakakin ‘yan sandan jihar, DSP Musa Mohammed, ya bayyana cewa an kama wasu da ake zargi kuma Sashen Binciken Manyan Laifuka na Jihar (SCID) na gudanar da bincike.

An kuma tsare direban motar da ake zargin maharan sun yi amfani da ita.