✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan daba sun fatattaki masu zanga-zanga a Legas

Zanga-zangar dai ta zama tashin hankali a wasu yankuna na Najeriya.

Wasu ’yan daba sun fatattaki masu zanga-zanga a yankin Alausa, inda ofishin gwamnati Jihar Legas yake.

Aminiya ta ruwaito cewa ofishin Gwamna Babajide Sanwo-Olu yana yankin Alausa, inda masu zanga-zangar suka yi cincirindo tun bayan fara zanga-zangar a faɗin kasar a ranar Alhamis.

Masu zanga-zangar sun ki komawa filin Freedom Park da ke Ojota, wajen da kotu ta amince musu su yi zanga-zanga a Legas.

Da misalin ƙarfe 12 na rana, wasu ’yan daba suka kai musu hari da makamai.

Masu zanga-zangar sun yi ta kansu, inda kowa ya cika wandonsa da iska.

Rahotanni sun ce jami’an tsaro da wajen ba su ɗauki mataki ba yayin da masu zanga-zangar suka tsere daga yankin.

Wannan lamarin ya faru ne bayan awanni 24 da ’yan daba suka hana masu zanga-zangar taruwa a filin Freedom Park da ke jihar.