✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Yajin aiki: Gwamnatin ta baiwa kungiyar ASUU Naira biliyan 15.4

Gwamnatin tarayyar Najeriya da Kungiyar malaman jami’o’i ta Najeriya ASUU sun yi tattaunawar  kulla yarjejeniya ranar Litinin akan yajin aikin gama  gari da kungiyar take…

Gwamnatin tarayyar Najeriya da Kungiyar malaman jami’o’i ta Najeriya ASUU sun yi tattaunawar  kulla yarjejeniya ranar Litinin akan yajin aikin gama  gari da kungiyar take yi.

Ministan qwadago na Najeriya Sanata Chris Ngige ne ya jagoranci tattaunawar da aka yi a Abuja.

Ngigie ya ce, sun kai karshen yarjejeniyarsu tsakaninsu da kungiyar ASUU, Gwamnatin tarayya baiwa kungiyar ASUU Naira biliyan 15.4 don kungiyar ta samu damar biyan albashi ma’aikata, wanda ya na daya daga cikin bukatun kungiyar.