✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Waiwayen Harkokin Wasanni A Shekarar 2013:Kano Pillars ta kafa sabon tarihi

A karshen makon jiya ne kulob din kwallon kafa na Kano Pillars da ke Kano wanda ake wa lakabi da “ Sai Masu Gida” ya…

A karshen makon jiya ne kulob din kwallon kafa na Kano Pillars da ke Kano wanda ake wa lakabi da “ Sai Masu Gida” ya kafa sabon tarihi bayan  ya lashe gasar rukuni-rukuni na Najeriya a karo na biyu a jere, kuma sau uku a tarihin kulob din.
Kodayake kulob din Lobi Stars da ke Makurdi ya doke na Pillars da ci 2-0 a wasan karshe a ranar Lahadin da ta wuce, duk da haka kulob din ne ya samu nasarar lashe gasar bayan ya hada maki 63 daga cikin wasanni 38 da ya yi.
Bayelsa United ce ta kasance ta uku bayan ta hada maki 61 yayin da El-Kanemi Warriors ta zama ta hudu da maki 60.