✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tsohon Shugaban EFCC Ibrahim Lamorde ya rasu

Lamorde ya riƙe shugabancin Hukumar EFCC daga shekarar 2011 zuwa 2015.

Tsohon Shugaban Hukumar Yaƙi da Yi wa Tattalin Arzikin Ƙasa Ta’annati (EFCC), Ibrahim Lamorde ya riga mu gidan gaskiya.

Lamorde ya rasu ne a birnin Cairo a ƙasar Masar inda ya je jinya kamar yadda aka sanar da safiyar yau Lahadi 26 ga watan Mayu.

Lamorde wanda ya rasu yana da shekaru 61, ya riƙe shugabancin Hukumar EFCC daga shekarar 2011 zuwa 2015.

Da farko dai an soma naɗa Lamorde daraktan ɓangaren ayyuka na EFCC lokacin da aka ƙirƙiro ta EFCC hukumar a shekarar 2003.

A watan Nuwambar 2011 kuma aka naɗa Lamorde a matsayin shugaban riƙon ƙwarya na Hukumar EFCC a zamanin mulkin Goodluck Jonathan.

Daga bisani an tabbatar da Lamorde a matsayin shugaban hukumar a watan Fabarairun 2012 har zuwa 9 ga watan Nuwambar 2015.

Bayan tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari ya yi nasarar lashe zaɓe a 2015, ya cire Lamorde tare da sauya shi da Ibrahim Magu a matsayin shugaban rikon ƙwarya na hukumar.

An haifi Lamorde a ranar 20 ga watan Disambar shekarar 1962 a jihar Adamawa inda ya shiga aikin ɗan sanda a shekarar 1986.