✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tsohon Kakakin PDP na kasa na ganawa da Tinubu a Aso Rock

Ya je fadar ne tare da Anyim Pius Anyim

Tsohon Sakataren Yada Labarai na jam’iyyar PDP ta kasa, Cif Olisa Metuh, yanzu haka yana ganawa da Shugaban Kasa, Bola Tinubu a fadar Aso Rock.

Metuh, wanda ya taba rike mukamin a PDP lokacin da APC ta kawo karshen mulkin jam’iyyarsa na shekara 16 a 2015, ya isa fadar ne tare da tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Anyim Pius Anyim.

A baya dai, duka su biyun sun shahara wajen yin adawa ga APC gabanin zaben 2015. An fara tattaunawar ce da misalin karfe 2:00 na ranar Laraba.

Shi kuwa Anyim, wanda kuma tsohon Shugaban Majalisar Dattijai ne ana ganin ya yi wa APC aiki a Jihar Ebonyi a zaben da ya gabata.

A watana Oktoban 2022 ne kuma Metuh ya bayyana ficewarsa daga PDP da kuma duk wata siyasar jam’iyya.

Wannan ne dai karo na farko da aka ga Metuh a fadar tun lokacin da tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan ya bar mulki.

A baya dai tsohon Kakakin ya fuskanci tuhuma kan zargin almundahanar wasu kudade, zamanin tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari.