✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tinubu ya bai wa iyalan wadanda aka kashe a Katsina kyautar 100m

Masari ya bukaci 'yan Najeriya da kada su bari wani ya ribace su da maganar talauci da rashin tsaro.

Gwamnan Katsina, Aminu Bello Masari, ya ce dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ya bai wa iyalan wadanda ’yan bindiga suka kashe a jihar kyautar Naira miliyan 100.

Masari ya bayyana haka ne a taron yakin neman zaben Tinubu a Katsina, inda ya ce gwamnatinsa na kokarin kawo karshen matsalar rashin tsaro a jihar.

A cewarsa, dan takarar ya bayar da kyautar kudin don rabawa iyalan wadanda ’yan bindiga suka kashe sannan ya yi addu’ar Allah Ya jikan mutum 40 da ’yan bindiga suka kashe a jihar a makon da ya wuce.

Masari ya ce, “Shugabanci ba abun wasa ba ne, yana bukatar jajirtattun mutane; Idan ka yi wasa da shugabanci na lokaci kalilan, to za a shafe shekaru ana shan wahala.”

A cewarsa, da gwamnatocin baya sun yi abin da ya dace yanzu ba a samu ’yan ta’adda irin Boko Haram ba.

Don haka ya bukaci ‘yan Najeriya da kada su yarda wani ya fake da matsalar talauci da rashin tsaro wajen neman kuri’arsu.