✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tinubu na ganawa da Akpabio da Jonathan a Aso Rock

A tattaunawar har da Ganduje da Uzodinma

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu yanzu haka yana ganawa sabon Shugaban Majalisar Dattajai, Godswill Akpabio, a fadarsa ta Aso Rock da ke Abuja.

Kazalika, cikin tattaunawar akwai Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma da tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje.

Shi ma Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu na tare da su a tattaunawar.

Gabanin haka, Shugaba Tinubu ya kuma gana da tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan a ofishinsa.

Sai dai har yanzu babu cikakken bayani game da makasudin duka ganawar tasu.

Shi ma shugaban Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) ya gana da Tinubun.