✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sojojin sun ceto mutum 13 da aka sace, sun kama mahara 11 a Zamfara

Sojojin sun mika mutanen da suka ceto ga wakilan gwamnatin jihar.

Sojoji sun ceto mutum 13 da ’yan bindiga suka sace, suka kama wasu mutane 11 dauke da makamai a Jihar Zamfara.

Mai magana da yawun rundunar Operation Hadarin Daji, Kyaftin Yahaya Ibrahim, ya ce ranar Lahadi ne sojojin suka fara aikin bincike da ceto mutane a yankunan Gobirawan Chali da Dangulbi da Dansadau a Karamar Hukumar Maru ta jihar.

Ya ce dakarun suka ceto mutum 13 da ’yan ta’adda suka sace a ranar daga kauyen Mutunji a karamar Hukumar.

“Duk wadanda aka ceto an mika su ga wWakilin Gwamnatin Jihar Zamfara don hada su da iyalansu.”

Sanarwar ta ce, “Rundunar ta gano maboyar ’yan ta’adda a Gidan Jaja a Karamar Hukumar Zurmi.”

Ya kara da cewa sojojin sun kama wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne 11 wadanda ke ba da kayan aiki ga wani fitaccen dan ta’adda Halilu Sububu a Kwanar Boko a Karamar Hukumar Zurmi.

“An kama wadanda ake zargin ne lokacin da suke dauke da buhunan hatsi 127 a cikin manyan motoci 2 na dan ta’adda Halilu Sububu. Amma a yanzu haka, ana bincike a kan su.”