✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sojoji sun rufe gidajen karuwai a Borno

Matakin na zuwa ne bayan wani rahoton Daily Trust.

Sojojin sun kai samame a wasu gidajen karuwai masu karancin shekaru da ke Kasuwar Fara a Rukunin Gidajen Shagari Masu Saukin Kudi da ke Maiduguri babban birnin Jihar Borno.

Rufe gidan karuwan ya biyo bayan wani rahoto na musamman da jaridar Daily Trust ta yi a ranar Asabar da ta gabata, inda ta bankado yadda ake tafka ta’asa a gidajen karuwai.

Mazauna yankin sun ce an kuma kama wasu mutane bayan “Sojoji sun kai samame wurin kwanaki biyu da suka wuce.

“Ba mu san inda suka kai masu laifin ba,” in ji wata mazauniyar yankin mai suna Halima Abdul.

Ta ce samamen da kuma sintiri da sojoji suka yi a yankin ya sanya al’umma cikin kwanciyar hankali.

“Mun sha wahala tsawon shekaru ana azabtar da mu amma da abin da muke gani yanzu kwalliya ta fara biyan kudin sabulu,” in ji ta.

Wani mazaunin yankin, Solomon Joseph, ya ce samamen da dakarun suka kai abin yabawa ne.

“Akwai ’yan kasuwa da suke sana’arsu a Kasuwar Fara, muna rokon sojoji da su bar su su dawo su ci gaba da harkokinsu,” in ji shi.