✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sojoji sun kama ‘yan kunar bakin wake 2 a Borno

Rundunar sojojin Najeriya na ‘Operation Lafiya Dole’ sun yi nasarar kama wasu ‘yan kunar bakin wake biyu mata da ke da shirin kai hari a…

Rundunar sojojin Najeriya na ‘Operation Lafiya Dole’ sun yi nasarar kama wasu ‘yan kunar bakin wake biyu mata da ke da shirin kai hari a kauyen Mushemiri a karamar hukumar Konduga ta jihar Borno.

A rahoton da sojojin suka fitar a shafinsu na twitter na cewa, an kama wadanda ake zargin masu yin kunar bakin waken ne a daren ranar Laraba lokacin da suke yunkurin kai hari sansanin sojojin a bataliya ta 222 da ke jihar.

Matan da aka kama duk su na daure da bamabamai a jikinsu .