✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sojoji sun ceto mafiya 16 da aka yi garkuwa da wasu a Filato

Dakarun Rundunar Operation Safe Haven ne suka ceto mutanen a cikin wata mota da a aka jefar da ita a yankin Mararabar Kantoma da ke…

Sojoji a Jihar Filato sun ceto wasu mutum 16 da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a kan titin Jos zuwa Mangu.

Dakarun Rundunar Operation Safe Haven ne suka ceto mutanen a cikin wata mota da a aka jefar da ita a yankin Mararabar Kantoma da ke Ƙaramar Hukumar Manngu.

Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, Manjo Samson Zakhom, ya bayyana cewa an ceto mutanen ne da misalin ƙarfe 9 na dare bayan sun tsinci motar a daji babu kowa a ciki.

Ya ce ganin haka ne sojojin rundunar da ke aikin tabbatar da tsaro da zaman lafiya a jihar suka yi zargin sace fasinjojin cikinta aka yi.

Manjo Samson Zakhom ya ce sojojin suna tsaka da bincike sai ’yan bindigar suka buɗe musu wuta, inda bayan arangamar ɓata-garin suka tsere suka bar matafiyan.

Ya bayyana cewa, a cikin fasinjojin 16 da aka ceto har da ƙananan yara guda shida, kuma duk a ba sau taimakon farko saboda raunukan da suka samu, sannan muka raka su, suka ci gaba tafiyarsu.”