Karamin Ministan Albarkatun Man Fetur, Dokta Ibe Kachikwu, ya zargi Babban Manajan Daraktan Kamfanin Mai na NNPC, Dokta Maikanti Baru da rashin biyayya da musgunawa.
Kachikwu ya yi zargin ne a wasikar da ya aike wa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari wacce ke dauke da kwanan watan ranar 30 ga watan Agustan shekarar 2017 wacce aka rika yada ta a kafar sada zumunta jiya.
Kamfanin mai na NNPC ya shelanta yi wa ma’aikatansa garambawul tare da nada manyan mukamai a ranar 29 ga watan Agustan shekarar 2017.
Ministan wanda ya jagoranci taron shugabannin kamfanin ya yi korafin a wasikarsa cewa babban manajan daraktan kamfanin bai sanar da shugabbanin kamfanin aniyarsa ta yi wa ma’aikatan kamfanin garambawul ba.