✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Shugaban kasar Namibia Hage Geingob ya rasu

A safiyar Lahadi Shugaba Geingob ya rasu a Asibitin Lady Pohamba da ke Windhoek, fadar gwamnatin kasar.

Shugaban Kasar Namibia, Hage  Geingob, ya rasu a sakamakon rashin lafiya yana da shekaru 82.

A safiyar Lahadi Shugaba Geingob ya rasu a Asibitin Lady Pohamba da ke Windhoek, fadar gwamnatin kasar.

Ya rasu a kan idon iyalinsa, kamar yadda mukaddashin shugaban kasa, Nangolo Mbumba ne ya sanar a Facebook.

Rasuwar tasa ta zo ne kimanin makonni uku da fadar shugaban kasar ta sanar cewa ya fara duba lafiyarsa saboda cutar kansa.

Sanarwar ba ta ba da karin bayani ba.

Daga baya ofishin Geingob ya ba da sanarwar cewa zai tafi Amurka don kula da lafiya kuma zai koma Namibiya a ranar 2 ga Fabrairu.

Geingob, ya kasance tsohon fira ministan kasar Namibia na tsawon shekaru 12.

Ya yi ta dama da rashin lafiya tun kafin ya zama shugaban kasar a shekarar Namibia na uku a shekarar 2014.