Kungiyar Dillalan Man fetur masu zaman kan su ta kasa IPMAN reshen Jihar Kuros Riba ta koka kan irin yadda wasu kamfanonin da ke sayar musu da albarkatun man fetur ke nuna halin rashin dattaku, a cewar Alhaji Isah Umar, daya daga cikin ’yan kasuwar da ya sayi kaya kan farashi, amma daga bisani saboda kayan farashinsa ya karu kamfanin da ya saya ya nemi tilasta masa sai ya dora kudin da suka karu bayan ya sayi kayan kafin ya dauka.
Alhaji Umar wanda yayi tir da halayen kamfanin sayar da mai na Samson dangane da karin kudin da yayi masa, ya sanya tilas ya biya, don haka a zantawar sa da Aminiya ya ce: “Abin mamaki na sayi man fetur kan farashi, amma da yake kafin in dauki kayan an samu karin Naira biyu akai sai kamfanin ya ce ba zai ba ni mai ba, har sai na dora wannan karin Naira biyu da aka samu akai kafin a ba ni kaya”. Lamarin dai dan kasuwar ya tubure kan cewa ba zai kara ko kwandala akai ba.
Ya ci gaba da cewa daga nan har matatar mai ta Warri idan aka sayi kaya indai kafin mutum ya dauka aka samu karin farashi ko da na sisin kwabo ne sai su ce sai mai kaya ya biya kafin a ba shi wanda hakan “ba adalci ba ne, “ inji shi. Wannan ja-ni-in-ja-ka da ke faruwa tsakanin Alhaji Isah Umar da kamfanin Samson masu daffon ajiye man fetur suna sayarwa da lasisin gwamnati ya tabbatar da cewa matukar ’yan kasuwa masu hali irin na wancan kamfani ba su sauya tunanin su ba suka rika kamanta gaskiya, to nan gaba fa ba za su kai labari ba.
D a wakilin mu ya tuntubi Mista Ugochukwu mataimakin manajan sayar da mai na kamfanin domin jin ta bakinsa game da lamarin ya zuke ya ce: “Ni ba ni da ikon yin magana da ’yan jarida, amma kayan su da suka saya za a ba su.” Sai ya kashe wayarsa.
Kamfanin mai na Northwest masu hada-hadar man fetur ne kadai suka ciri tuta a wajen kamanta gaskiya a harkokin su na kasuwa, kamar yadda Alhaji Isah Umar ya tabbatar wa manema labarai da suka garzaya kamfanin domin jin yadda lamarin ya gudana tsakanin su.