dan kwallon Liberpool Sadio Mane yana daga cikin al’ummar Musulmin da ke yin dawainiyar wanke bayin Masallacin Ar-Rahman na Liberpool da ke Ingila.
Kamar yadda wani faifan bidiyo da aka watsa a kafofin sadarwar zamani ya nuna, an ga Mane dauke da bokiti yana hidimar wanke bayin Masallacin Liberpool da kuma wurin da ake yin alwala.
An ce dan kwallon ya shiga hidimar wanke bayin ne jim kadan bayan sun tashi wasa a tsakanin Liberpool da Leicester City, inda Liberpool din ta doke City da ci 2-1 kuma Mane yana daga cikin ’yan kwallon da suka zura kwallo a raga.
Sadio Mane yana daga cikin ’yan kwallon da ke yin sujada a filin kwallo a duk lokacin da suka zura kwallo a raga da hakan ya nuna yana da kishin addinin Islama.
Masana harkar kwallon kafa a ciki da wajen Ingila sun yaba wa dan kwallon game da hidimar da yake yi wa Masallaci musamman a matsayinsa na shahararren dan kwallon kafa.