✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Rarakar rububin rudani

Alhini An nuna mini aikin hauni Artabun zubar da jini An zubar da rayuwar wani An tsaya ana ta wuni-wuni   Rarakar rububin rudani Rotsi…

Alhini

An nuna mini aikin hauni

Artabun zubar da jini

An zubar da rayuwar wani

An tsaya ana ta wuni-wuni

 

Rarakar rububin rudani

Rotsi da rauni

Rayuwa ta samu hautsini

Rudun rashin sani

Rashin riga da rawani

 

Batun ga akwai sarkakiya

babatun sasarin soyayya

Soyewar zukata ko kiyayyya

Kurtun Magana ya haifar da jayayya

Kisan wuka babu jinya

 

‘Yar bora

Ta rasa mamora

Salwantar da rai babbar asara

Tarin dami kan zabge da zara

Shi ya aka kai makura

 

’Yar mowa

A gidin murhu tana da uwa

Ta aza sanwa

Ta yi ta kwankwadar gahawa

Babu mai yi mata tsawa

 

Shi ma danlele

Ai ya yi male-male

Shishar dan malele

An bar mu muna ta kalle-kalle

daukar hankali da kyale-kyale

 

 

Marigayi dan Bello

Bibiyar kurtun halo alalo

Matarsa ta sha kallo

Sakonnin mata salo-salo

Sun yi tsiyakun karin kumallo

 

Labarai ne aka kalato

Jaridu ne suka ruwaito

Mahukuntan fuskantar boko

Tukin tuwon titin damun koko

Kowa ya sassauto

 

An bar aura ana jibgar taiki

Innar Mairamu ta hadu da masu baki

Wai babanta ne mutumin kirki

Alhali shi yai sakaci bayan saki

Sarayar da zuri’a ne rugujewar daki

 

Mace na da rauni

Miji ya zam da kaifin tunani

Ban da sakarci a sansani

Yasar da ta’adun iyaye da kakanni

Muna ta yi wa juna gani-gani

 

Yanzu masu taku da kulki

Sun bazama kan aiki

Bincike ne daki-daki

A daina kintace ba burki

Kada miya sai da maburki

 

Iyaye da ’ya’ya

Ku sauke wa kanku kaya

Hakkokin da suka rataya

A bayar da bayayya

A kiyayi tsiya-tsiya

 

A gurfana gaban alkali

Shi kuwa ya zamto adali

A yi hukunci na hankali

Kar a kyale mai fetali

keke-da-keke ai tozali

 

Cusa haushi

Ke haiufar da saurin fushi

Har a kai ga naushi

Da sukewar numfashi

Gaba babu fashi

 

Mu zamto masu da’a

Mutanen da ke kyautata dabi’a

Munanan ayyuka mu ce musu a’a

Kowa ya kiya yi masha’a

Mu daina yi wa juna ba’a

 

karshen makon da ya race an yi ta baza batutuewa bambarakwai kan kisan gillar dan Bello, wani matashi da ake ce mahaifinsa ya taba zama babban jigo a Jam’iyya mai dan boto da sanda jirge, kuma an yanke cewa mai dakinsa ce ta tsira mas tsitaka har ya ce ga garinku nan. Mafi yawan batutuwan dai a shafukan FUSKANTAR BOKOKO da na TUkIN TUWON TITI aka yi ta kwararo su, inda a kodayaushe akla zo sake jigba wa mai dakin dan Bello laifinm kisan gilla sai an Ambato mahaifiyarta, har ta kai ga ana ta nuni da cewa, mahaifint amutumin kirki ne, amma uwar ta yi hannun riga da ayyukan kwarai. Ni dai na fasko cewa, ‘mafi yawan al’amuran da aka ruwaito a kafafen sandarewar surutun sadarwa kawai RARAKAR RUBUBIN RUdANI ne.

Haurobiyawa matukar muna son tabbatar da adala sai mu tuhumi Mairamu da ta’asarta a kwanon tasarta, amma kada mu yi fafutikar mayar da ita ’YAR KUKA. Kuma ai shi ma mahaifinta wani katabus ya yi bayan ya sallama mahaifiyarta? To a bar kaza cikin gashinta; idan kuwa aka ci gaba da tone-tone to allura za ta tono garma,’ ta yadda masu laluben gararuma za su karke da gardama, a dinka mussu gumama su yi ta hauma-hauma.

Ina ganin bai dace mu yi ta ce-ce-ku-ce ba, musamman jin cewa masu taku da dan kulki dakon giwa tsagiya bugu da kari sun bazama wajen bincike, sai mu daina kawo musu tarnaki don su hanzarta wulwula takunb fedar keke, tunda su aka dora wa alhakin leke-leke, har a kai ga gaban alkali adali, wanda ba ruwansa da shafaffe da mai zanen fetali, har a tabbatar an yi keke-da-keke wajen tunkarar wannan matsala, inda daukacin masu ruwa da tsaki za su taho ai tozali.

Lallai a dainma shaci-fadi ko zantuttuka da yawan kaudi kamar rawar dodon kodi. Kuma na gargadi masu yada rade-radi, don gudun kada su haifar wa al’umma radadi. Wannan lamari ne na karon battar ’YAR MOWA da BORA

’Yan makaranta masu koyon watsattsake da buda wwagagen littattafai da mujallu da makalu da jaridu, babban abin nussarwa a wannan takammar kisan gilla da ake zargin Mairamu da salwantar da rayuwar danBello, shi ne daukacin wadanda ake ta RARAKAR RUBUBIN RUdANI a kansu, lallai duk miyagun dabi’un da suka bayyana wani ya aikata koda banker hayakin tabar SHISHA ce ko caka wa maigida TSITAKA har y ace ga garinku, mu yi kokarin kauce wa kwata mummmunan aikin da ya jefa jama’a cikin jimami ha rake ta alhinin zubar da jini, ta hanyar aikin hauni ko tsira tsinin tsitaka ta haifar da raunin da ya jawo jayayya ana ta kayya-kayya tun kafin a akai aya wajen gano yadda wannan matashi ya ce ga garinku ba tare da jinya ba. Haurrobiyawa mu yi kokarin tantance TSABA DA TSAKUWA, ta yadda kowa zai fasko masu yi mana kuwa suna daka wawa don mu rika yin tsuwwa.