✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

PDP ta yi wa Buhari raddi kan rashin kiyaye matakan dakile cutar Coronavirus

Buhari ya yi abun kunya a matsayinsa na Shugaban Kasa.

Babbar jam’iyyar adawa a Najeriya PDP ta ce saba wa matakan kariyar COVID-19 da Shugaba Muhammadu Buhari ya yi yayin sabunta rajistarsa ta jam’iyyar APC abun kunya ne a gare shi.

PDP ta bayyana haka ne cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Lahadi, wadda ta ce abin da Buhari ya aikata abun kunya ne.

Jam’iyyar ta ce rashin kiyaye dokokin da mahukuntan lafiya suka shar’anta domin dakile yaduwar annobar Coronavirus da Shugaba Buhari ya yi babban abun kunya ne.

“Tabbas abun kunya ne a ce a yayin da ’yan Najeriya ke kokarin kiyaye matakan kariyar COVID-19, amma Shugaban kasa ya karya dokar yayin da yaje sabunta rajistar jam’iyyarsa a Daura, Katsina.

“Kafofin sadarwa sun nuna yadda hotunan shugaban kasa suka karade yana tattaunawa da shugabannin jam’iyyarsa, ba tare da takunkumi ba, bare bayar da tazara,” a cewar PDP.

Jam’iyyar ta kara da cewa babban abun kunya ne ga shugaban da yanke hukuncin wanda ya karya dokar matakan kariya, a kuma same shi ya karya su kwanaki biyar bayan sanya wa dokar hannu.

A ranar Asabar ne Shugaba Buhari ya sabunta rajistarsa ta jam’iyyar APC, a mazabar Sarkin Yara da ke garin Daura a jihar Katsina.