✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Najeriya ta yi wa Sao Tome dukan raba ni da yaro

A wasan farko da Najeriya ta je gidan Sao Tome a karawar rukunin farko, ta yi nasarar cin 10 – 0 ne.

Tawagar kwallon kafa ta Najeriya ta doke ta Sao Tome 6-0 a wasan neman shiga Gasar Kofin Afirka da suka kara ranar Lahadi a Uyo, Jihar Akwa Ibom.

Minti na 13 da fara wasa Super Eagles ta fara cin kwallo ta hannun Victor Osimhen, sannan Ademola Lookman ya ƙara na biyu minti na 14 tsakani.

Bayan da suka koma zagaye na biyu ne ɗan wasan Nottingham Forest Taiwo Awoniyo ya ƙara na uku a raga.

Najeriya ta ci kwallo na huɗu a bugun fenariti, kuma Osimhen ya zura a raga wadda ita ce cikon ta tara da ya ci a wasannin neman shiga Gasar Kofin Afirka.

Haka kuma shi ne ya ci na biyar na uku rigis a fafatawar, sannan Samuel Chukwueze ya ci na shida, saura minti huɗu a tashi daga gumurzun.

A wasan farko da Najeriya ta je gidan Sao Tome a karawar rukunin farko, ta yi nasarar cin 10 – 0 ne.