✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Najeriya ta koma amfani da tsohon taken kasarta

An sauya taken Najeriya daga 'A rise O compatriots' zuwa 'Nigeria we hail thee.'

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu kan dokar komawa amfani da tsohon taken Najeriya.

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio ne ya sanar cewa shugaban kasar ya sanya hannu kan dokar a ranar Laraba.

A ranar ce Shugaban Tinubu kai ziyara zauren majalisar inda ya jagoranci sake kaddamar da tsohon taken Najeriyan da aka dawo da shi.

A bisa sabuwar dokar, taken Najeriya da ya fara da ‘Nigeria we hail thee,’ zai ci gaba aiki; shi kuma , ‘A rise O compatriots’ zai koma masayin addu’ar kasa.

Shugaban kasar ya bukaci majalisar ta hada kai da bangaren zartarwa domin amfanin al’ummar kasar.

Da yake wa al’ummar kasar murnar cika shekaru 25 a karkashin mulkin dimokuradiyya babu yankewa, shugaban kasar ya yi kira al’ummar kasar kada su kawo nakasu ga tsari.